I Z A L A@el_uthmaan
HADISIN IMAM MUSLIM NA AZUMIN SITTA SHAWWAL BAI INGANTA BA
Imam Malik da Abu Hanifa sun karhanta azumi 6 na watan Shawwal, wanda bayani zai biyo baya in sha Allah game da dalilinsu na karhantawa. Wannan magana tabbatacciya ce kuma sananniya ga wanda yake da alaka da ilimi.
Amma wanda suka ce babu karhanci sun dogara ne a kan Hadisin Imam Muslim dake Musnad dinsa. To ga bayani da sunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai.
«المفهم لما أشكل من تلخيص كتاب مسلم» (3/ 239):
«قلت: وحديث أبي أيوب المتقدم، وإن كان قد خرَّجه مسلم ليس بصحيح، وهو من جملة الأحاديث الضعيفة الواقعة في كتابه؛ وذلك لأن في إسناده: سعد بن سعيد بن قيس؛ قال فيه النسائي: ليس بالقوي، وغيره يضعفه، كما ذكره الترمذي، وقد انفرد به عن عمر بن ثابت، قال أبو عمر بن عبد البر: أظن أن الشيخ عمر بن ثابت لم يكن عند مالك ممن يعتمد عليه.
Al-Qurduby a cikin littafin “Al-Mufhimu lima Ashkala min Talkhisi Kitabi Muslim” (3/239), ya ce:
“Na ce: Hadisin Abu Ayyub al-Ansari da ya gabata, duk da cewa Imam Muslim ya ruwaito shi, ba sahihi ba ne. Yana daga cikin hadisan da suke da rauni da suka zo a cikin littafinsa. Dalilin haka shi ne: a cikin isnad ɗinsa akwai Sa'd ibn Sa'id ibn Qays; An-Nasa'i ya ce a kansa: ‘ba mai ƙarfi ba ne,’ wasu kuma suna raunana shi, kamar yadda Al-Tirmidhi ya ambata. Kuma shi kaɗai ya ruwaito shi daga Umar ibn Thabit. Ibn AbdilBarr ya ce: Ina zaton Sheikh Umar bn Thabit bai kasance a wurin Imam Malik daga cikin waɗanda ake dogaro da su ba.
Sannan daga cikin raunin Hadisin a matani shine zuwan kalmar ستا memakon ستة:
وإنما أنَّث (ستًّا)، وكان حقها أن تذكر من حيث: إن الصوم إنما يوقع في الأيام، واليوم مذكر.
"Kuma an yi amfani da lafazin mace (‘sittan’ – shida) alhali daidai shi ne a zo da lafazin namiji, saboda azumi ana yi ne a cikin yininnika ne, kuma ‘yini’ (a larabci) namiji ne."
Wannan magana ta Al-Qurduby cewa an samu kuskure a Larabcin Hadisin, alhali Annabi SAW yafi kowa iya larabci ya nuna rauni a hadisin.
Mufti Sheikh Dr Ahmad Gumi sanda ya fadi wannan maganar, sai azzaluman salafawan nan suka ce wai Dr Ahmad Gumi ya ce Annabi SAW yayi gwaranci a larabci. Allah ya saka masa na wannan sharri da yarfe da suka masa.
Irin wannan ya faru a Hadisin Ka'ab b. Malik inda yace:
وآتي رَسولَ اللهِ صلَّى اللهُ عليه وسلَّم فأُسَلِّمُ عليه وهو في مَجلِسِه بَعدَ الصَّلاةِ، فأقولُ في نَفسي: هل حَرَّكَ شَفَتَيه برَدِّ السَّلامِ عليَّ أم لا؟
"Na kan zo wajen Manzon Allah SAW in masa sallama yayin da yake majlisinsa bayan sallah, a cikin rai na sai nace: shin labbansa sun motsa don maida min sallama kuwa ko basu motsa ba?"
Malamai suka ce cewa أم لا din nan ya nuna cewa Hadisin ya gaurayu da ajamawa. Larabawa basa yin haka, kamar yadda muka gani a wurare da yawa a cikin Qur'an, misalin fadin Allah:
قل هل يستوي الذين يعلمون والذين لا يعلمون؟
Allah bai ce أم لا ba.
Irin wannan illa a matani tana nuna rashin tabbatuwar maganar da da rashin kwarewar wanda suka dauko ta. Sabida haka ba a samun ilimin yaƙini Annabi ne ya fada.
Imam Al-Bukhari bai yi riwaya ko daya daga mutumin nan سعد بن سعيد بن قيس ba. Annawawy cikin Sharhin Muslim yake cewa:
«شرح النووي على مسلم» (1/ 16):
«عدد من خرج لهم البخاري في الجامع الصحيح ولم يخرج لهم مسلم أربعمائة وأربعة وثلاثون شيخا وعدد من احتج بهم مسلم في المسند الصحيح ولم يحتج بهم البخاري في الجامع الصحيح ستمائة وخمسة وعشرون شيخا»
A cikin شرح النووي على مسلم (1/16):
“Adadin malamai da Bukhari ya ruwaito daga gare su a cikin littafinsa Al-Jami'u As-Sahih, amma Muslim bai ruwaito daga gare su ba, sun kai malamai 434.
Haka kuma, adadin malamai da Muslim ya kafa hujja da riwayoyinsu a cikin littafinsa Al-Musnad As-Sahih, amma Bukhari bai dogara da su ba a cikin littafinsa, sun kai malamai 625.”
Dalilin wannan kuwa shine abinda Annawawy ya fada cewa idan Bukhari yaƙi riwaye daga wanda Muslim yayi riwaya daga gare shi, domin Bukhari bai yadda da mutumin bane cewa sharuddan karban Hadisi sun cika tare da shi. Haka shima Muslim.