Kwankwasiyya Reporters@KKSY_Reporters
WANENE MATSALAR; Kwankwaso ko Atiku?
Madugu yana cikin jam’iyyar ADC, amma tun farko Atiku ya fara nuna adawa da shi. Aka ce wai farin jininsa iya Kano ne kawai, sannan yanzu kuma ake cewa kuri’unsa sun ragu saboda wasu sun bi gwamnan Kano sun bar shi. Duk irin kalaman da Atiku ya yi, magoya bayansa ma haka suke ta maimaitawa a kullum.
Yanzu da Madugu ya fita ya bar su, sai suka koma zage-zage da yi masa kallon marar kishin Arewa. Wasu suna cewa wai ya ci amanar jama’a, wasu kuma suna cewa ɗan kwangila ne ko kuma yana yi wa Tinubu aiki.
Tambayoyin da da ya kamata a yi sune:
1. Shin Kwankwaso ba shi da ‘yancin yin abin da yake ganin ya dace da rayuwarsa da kuma makomar magoya bayansa?
2. Mutane da dama a Arewa, har da gwamnoni, sun ƙi bin Atiku zuwa ADC. Misali, Gwamnan Adamawa bai bi Atiku ba. Me yasa ba a zagin su kamar yadda ake yi wa Madugu?
3. Ko Najeriya mallakin ‘yan Arewa ce kawai?
4. Tunda kunce iya Kano ne ake son Kwankwaso menene na damuwa idan ya fita?
5. Atiku yana ina lokacin da Kwankwaso yake fita domin kare yan Arewa da Arewa?
6. Ta wacce hanya zaku iya gamsar da mutane cewa Atiku yafi Kwankwaso kaunar Arewa?
Madugu, matuƙar yana raye, ba za ku taɓa raba shi da masoyansa ba. Saboda irin alkhairin da ya shuka tsawon shekaru a Najeriya ba abu ne mai sauƙin gogewa ba. Wannan ne yasa mutane suke son sa da zuciya ɗaya, ba tare da wata tilas ba.
Madugu ba ya gudun jama’a. A kullum yana cikin Najeriya; idan ba a Abuja yake ba, to yana Kano. Yana halartar gaisuwar mutuwa, ɗaurin aure, jajen rashin lafiya, da sauran harkokin al’umma. Kofarsa a buɗe take domin ganin jama’a, ba irin mutanen da suke guduwa zuwa Dubai ba sai lokacin zaɓe ya yi sannan su dawo.
Ba ya amfani da kuɗi wajen sayen mutane, kuma bai yarda cewa kuɗi ne kawai ke kawo farin jini ba.
Yana tsayawa tare da magoya bayansa domin kare martabarsu, tare da ƙoƙarin ɗaga darajar talakawa da inganta rayuwarsu.
Saboda haka, ban ga wata hanya da za a iya bata Madugu a idanun masu hankali ba. Duk inda ya dosa, za mu bi shi, domin mun yarda da jagorancinsa na adalci da gaskiya.
Comrade Abdullahi Ghali Basaf
10/05/2026